Afrilu 10 Ga wata Bahari Ya Kara Na Wa'adin Karbar Kudi

ZANGO MEDIA
0


Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya bai wa babban bankin ƙasar umurnin ya sake fito da tsofaffin takardun naira 200 domin a ci gaba da mu'amala da su a ƙasar.

Shugaban ya bayyana haka ne a cikin jawabin da ya yi wa al'ummar ƙasar da safiyar yau Alhamis.

Buhari, wanda ya ce yana sane da irin halin wahala da al'ummar ƙasar ke ciki, ya ce za a ci gaba da amfani da takardar kuɗin ta naira 200 har zuwa 10 ga watan Afrilu.

Ya kuma buƙaci al'umma da su ƙara haƙuri kan halin da ake ciki.

Za mu kawo maku ƙarin bayani kan bayanin shugaban ƙasar.

BBC HAUSA

Post a Comment

0Comments
Post a Comment (0)