Ko Ya Makomar Gwamnan Kano Ganduje

ZANGO MEDIA
0

Tun bayan zaben shugaban ƙasa a jihar Kano inda jam’iyyar APC mai mulki ta sha kaye a hannun jam’iyyar adawa ta NNPP, alamu suka nuna cewa gwamnan jihar Abdullahi Umar Ganduje sai ya dage idan har yana son ɗan takarar APC, Nasiru Gawuna ya ci zabe.

Amma bayan kammala zaɓen gwamna a ƙarshen mako, sai jam’iyyar NNPP ta kwace ragamar jihar inda hukumar zabe ta ƙasa INEC ta ayyana Abba Kabir Yusuf a matsayin wanda ya lashe zaben gwamnan jihar.

Wannan sakamakon ya nuna cewa Ganduje bai kawo jiharsa ba ga jam’iyyar APC a zaben gwamna da kuma na shugaban kasa.

A yanzu ta tabbata cewa a cikin watan Mayu jam’iyyar NNPP ita ce za ta shiga fadar gwamnatin jihar Kano a yayin da APC za ta koma adawa.


BBC HAUSA

Post a Comment

0Comments
Post a Comment (0)